Complete Hausa Novels

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 32 of 227

This is the second reason da yake son zuwa gurin Hajiya Jamila kullum kofar falonta a bude take not like gidansu da sai danna ko ka yi knocking za a bude maka, talkaminsa ne abun da ya fara cirewa sannan ya shiga falon. Hajiya Jamila dake zaune kam carpet rike da carbi ta dago ta idonta dake sanye da gilashi ta kalleshi, a take annashuwa da farinciki suka wanke zuciyarta har suka kasa boyuwa sai da suka bayyana a fuskarta.

“Ameer... Dana....”

Ta fada tare da aje carbin ta mike tsaye ta cire gilashin ta bude masa hannayensa tana masa alama ya karaso gareta, sai ya tsaya yana kallonta.

“Akwai datti a jikina sosai i can't hug you like that, idan na fada miki wahalar da na sha sai kin yi wahala”

Ita da kanta ta karasa inda yake tsaye ta rumgumeshi.

“Ban taba jin kyamarka ba ďana, ba zan taba kyamarka ko kuwa datti duniyar nan zai tabbata a jikinka ne”

Maganar take hawaye na sauko mata, shi kansa ya san Hajiya Jamila tana matukar kaunarsa, kamar yadda yake kaunarta sosai a ransa domin mahaifinsa ya fada masa ita ce second macen da nononta ya kai cikin cikinsa bayan mahaifiyarsa.

“I miss you so much Ammyna and i Love You”

“I love you more Son”

Shi ma rumgume ta yayi sannan suka nufi kujera suka zauna tana rike hannunsa, wani irin kaunarsa take kamar ta bude zuciyarta ta saka shi ta rufe ta hana kowa iko da shi sai ita kadai.

“Ina ka je Ameer?”

“Daddy ya kira ni?”

“Ya kira ni, kuma hankalina ya tashi sosai, Ameer ashe ni ba mahaifiyarka ba ce idan Mr Bashir ya koreka ba zaka iya guduwa ka zo gurina ba? Ka daga min hankali sosai ina ta fargabar abun da ya same ka, duk inda na san zaka iya zuwa na bincika amman ban san samu ka ba, Wayoyinka duk a kashe”

“Ance Daddy be da lafiya da gaske ne?”

Ta daga masa kai.

“Kuma Saboda kai ne Ameer, ni yanzu na yanke shawara tun da har matsala kuke samu zaka zauna a gurina shi kuma sai ya zauna a can tare da matarsa da yayansa, daman ni bana ni da kowa sai kai, kai kadai nake da Ameer Allah be bani kowa ba sai kai kadai”

Jikinta har rawa yake tana taba fuskarsa, akwai wani irin rauni da tarin damuwa a gurin macen da girma ya kamata kuma bata ganin sanyin idaniyarta ba, bata da wani ďa na cikinta sai dan ya sha nononta kamin girma.

“Ina da duk wani abu na jindadin rayuwa da zan baka Ameer, kuma zan jidadi idan ya zabi zama a nan, ko ba komai mahaifinka zai samu space kuma za su daina fada da juna”

“Ammyna kin san ina sonki, amman ba zan iya zama a Kano ba, rayuwata gaba daya a Abuja nake yinta musamman a yanzu da ya kamata na dauki fansa, mun saba na kan zo na dubaki ke ma kuma kina zuwa dubani idan kika yi marmarina”

“Haka ne”

Ta fada ba dan ranta na so ba, sai dan ya zame mata dole ta so abun da yaron da take kallo a matsayin ďanta yake so, tana da ƴaƴan yan'uwa da take riko maza da mata amman bata son kowa kamar yadda take son Ameer saboda ya sha nononta shi ne kadai ďan da ta shayar a matsayin nata ta rumgume shi a hannunta ta yi masa duk wata hidima da uwa take yi ma ďanta.
Ya mike tsaye tare da cire rigar jikinsa

“Ina yan matan gidan nan?”

“Basa nan kasan an koma makaranta duk suna makaranta, bari na shirya maka abun da zaka ci kamin ka yi wanka”

“I hope my room is clean”

“Kullum dakinka a gyare yake Ameer, kullum ina sakawa a gyara shi a saka turare saboda ina saka ran zuwanka a ko da yaushe kamar yadda kake yi ba tare da ka fada min ba”

Yayi murmushi sannan ya nufi hanyar fita falon domin dakinsa ba a cikin part dinsa yake ba, gidan kuma ba bakonsa ba ne.

MALEEK POV.

“No ba sai kin zuba min ba, zan karya tare da yarana”

Abiey ya dakatar da Ummi a kokarinta na zuba masa ruwan zafin da suke ta kamshi. Dagowa ta yi ta kalleshi doguwar riga ce a jikinsa har yanzu babu annuri a fuskarsa, dawowar da yayi ma bayan kauracewa gidan ta yi tambayarsa dalilin haka sai ya fada mata ba komai aikine ya biyo da haka, yanzu kuma yana kokarin kauracewa abincinta.

“Fushi ne har yanzu ranka ya dade?”

“Ke fa kika fada min cewar mu ba yara ba ne a yanzu, to mi zai saka mu yi ta abu kamar yara?”

Yaja kujerar daya saba zama ya zauna, daman ya saba ya kan yi breakfast tare da yaransa irin weekend haka ita kuma ta yi da yan matansa, saboda Maleek da baya kaunar zama kusa da mace ko jin muryarta ko da kuwa mahaifiyarsa ce balle kuma kanenesa sai dole, idan har ana son aga sakewarsa sai idan an bar shi ya kebe da maza yan'uwanshi ko kuma mahaifinsa da kanensa, wannan ya saka Abiey ya ware musu gurin karyawa ko yin lunch saboda Maleek. Ta bude baki zata yi magana Mahmood ya shigo falon sai ta yi saurin hade kalamin ta dauke hannayenta daga teburin ta nufi kofar fita, hakan yayi daidai da shigowar Maleek matsawa yayi gefe domin ya bata hanya ta fita, secondly kuma baya son jikinsa ya taba nata. Tsayawa ta yi kallonsa shi kuma ya sauke kai kasa.

“Ina kwana?”

Bata amsa masa ba sai ta tambaye shi abun da ya fi tsaya mata a rai.

“An gano inda Abokin ka yake Maleek?”

“I don't think so”

In a very law voice ta yi masa maganar, amman hakan be hana Abiey jiyo abun da take tambayar ďansa ba, domin hankalinsa gaba daya yana kansu.

“Ina matukar kaunar yayana, hakan ya saka nake kaunar farincikinsu, ko kadan bana son abun da zai daga hankalinsu ko ya saka su a damuwa”

Ko be ambaci sunanta ba ta san da ita yake, jiyowa ta yi ta kalleshi sai kuma ya juya ta fice ba tare da tace komai ba, fuskar mamaki Mahmood yayi ya kalli mahaifinsa sai dai be ce komai ba, Maleek kuma yayi zaton saboda Ummi ta tsaya a kofa ne ya saka Abiey fadin haka sanin baya son kusanci da mace sai dole.
Kuskus Ummi ta samu Nimra da yar'uwarta na yi, suna ganinta sai suka daina Namra ta shiga hadawa kanta Tea Nimra kuma ta saka taba komai, sanin cewar tsakanin Uwa da ya ana sirri haka aboki da aboki balle kuma dan'uwa da yar'uwa ya saka bata damu ta san abun da suke tattaunawa akai ba, sai dai ta damu matuka da damuwar da take gani a fuskar yarta Nimra, domin abu ne data kasa boyewa gaba daya mu'amalarta da annashuwarta basa tare da ita yanzu, a baya kuma ba hala take ba, da m Namra ce ba za a gane idan tana cikin damuwa ba domin ita bata sakewa da mutane kuma bata da yawan far'a da raha ba kamar Nimra ba. Ummi da kanta ta zuba mata tea ta aje mata komai sannan taja nata kujerar ta zauna, no matter how take jin damuwa idan ta ga yaranta a cikin wata damuwar sai nata damuwar ya gushe. A hankali Nimra ta kai ta fara cin abinci gaba daya jin sa take kamar dusa ba domin ba abincin ne a ranta ba, Ameer take tunani ko a wane hali yake a yanzu, ta san yana raye saboda alert din da ta gani na kudin da aka cire a ATM din data bashi sai dai har zuwa yanzu wayar bata shiga idan ta kira. Idan ya dawo ya za'ayi ya yarda da ita? Shi ne babbar damuwarta a yanzu, and miyasa take damuwa da haka shi ya zama third damuwa a gareta.
Misalin karfe biyu da rabi na rana Nimra na zaune falo not knowing what to do, Namra kuma bata gidan ta fita gurin aikinta Mahmood na zaune a dinning tare da Ummi, yayinda mai aikinsu take aikin aje manyan warmers a dinning din, Abiey ya shigo hannunsa rike da waya Maleek na bayansa. Ummi na ganinsa sai hankalinta dana Mahmood ya koma kansa domin be a yanayin da ke nuna lafiya ta kawo shi, Nimra ma tashi ta yi zaune.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.