Complete Hausa Novels

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 218 of 227

Ranar laraba aka fara gudanar da shagulgulam auren a event center daya, tun farkon fitar pre-wedding pictures mutane suka fara maganar auren mata shida maza shida, musamman ma yadda suka sha kyau da tufafi masu burgewa. Kowa da yanayin yadda yayi nasa hoton sai dai babu wadanda aka fi yabawa kamar Maleek da Nuwaira domin su ne kadai suka yi hoto ba tare da taba juna ba, Maleek ko hannun Nuwaira be yarda ya rike ba, gashi sun wanku fess kamar wasu labaraba musamnan a inda take saka lifaya da inda suke tsayuwa gurin doki shi da kuma gurin da ya saka alkibba ita ma ta saka sai kuma girin da ta saka farin lace shi kuma ya saka farar shadda, duk inda za a ace su kalli juna Nuwaira sai ta daga kai take kallon Maleek domin bata tsawo sosai kuma ba zaka ce mata gajera sosai ba, kana kallonta kasan ita kadai ce yarinya a cikin manyan yan mata. Ba kamar Humairah da Ameer ba domin shi kadan ya darata tsawo, wani gurin ya rika hannunta wani gurin kuma ya rike kunkurunta wani hoton kuma ya dora hancinsa a nata, babu kalar rigimar da Humairah bata yarda yi ba kamin ya shawo kanta daker ta yarda, wani hoto kuma ita da shi sun juya baya suna kallo mai daukar hoton dukansu sun yi murmushi kana ganinsa kasan yan'uwa ne domin suna kama da juna musamman a yanzu da Humairah ta kile wuyanta har wani zane yayi an mata dilka ta ci abinci mai kyau kuma hankali ya kwanta domin ta samu abun da take so.

Ummi ta girgiza kai bayab ta gama kallon video bikin da aka yi na yau thursday wato bride and groom Day, wani sabon event da ake yi kawayen Amarya kawai ke zuwa sai ango da friends dinsa ayi ta ruwan kudi ana chashewa. Maleek dai be yarda yayi rawa ba, daman shi irin ababen nan ba su cika burge shi ba, zuwan ma dan ya zame masa dole ne, Ameer ya daka rawa abunsa Humarah ce dai bata yi rawa ba domin ita ma tana da kunya, Namra da kanen Ameer ma sun yi rawa da yan matansu Shuraim ma ba da ba zaka ce zai aikata ba haka ya zage dantse yayi ta rawarsa friends dinsa suna ta masa ruwan kudi.

“Kin ga ďan nan naki be cika kunya ba Ummi”

“Kai wa san abun da zaka yi idan an tashi auren”

“Ni ma ai kin san rawa zan yi Ummi rana irin wannan ba ko da yaushe take dawowa ba, kuma idan ma ta dawo wata kila na yi girman da ba zan iya yin rawar ba”

Ummi ta gigiza kai tana kallonsa da murmushi.

“Ba mata daya zaka yi ba kenan?”

“Aa gaskiya ni ba irin Abiey ba ne, mata uku ma zan yi kin ga ina son na tara yara da yawa, kuma ni ina sha'awar auren mata biyu ko uku”

“Kai da har yanzu ma baka samu matar auren ba sai ruwan ido kake? Da yanzu an hade aurenka da yan'uwanka”

“Aa ni nafi son nawa ni kadai, kuma sai na zaba na darje kar na yi zaben tumun dare”

“Allah ya shirya ka kuma ya nuna mana yasa ina da rabon gani”

“Zaki gani Ummi In Shaa Allah”

Ta dade tana hira da danta sannan ta tashi ta fita cikin mutane. Kusan babu gidan tv da be haska dauren auren da aka yi a babban Masallaci Jumma'a dake Abuja ba, domin daurin aure ne da ya samu halartar manyan mutane lungu da sako na nigeria har ma da waje kasar. Daga bangaren Daddy da Abiey sai kuma bangaren Shuraim da kuma surukan Daddy da suka kasancewa manyan mutane. An yi ma Abiey kara haka ma Daddy an masa kara domin daurin aure ne na farko da kowa wannen ya fara yi, kuma sun halarci na wasu dole su na ayi musu a nasu ko dan Naira... Bayan saukowa daga Sallah Jumma'a aka daura auren Maleek da Nuwaira, Ameer da Humaira, Namra da Shuram, Ramla da Yunus, Afrah da Aliyu, Bilqis da Mu'azzam ƴaƴan Mr Bashir.

Baya daurin auren aka yi liyafar cin abinci babbar hotel din Fancy Home dake Abuja, babbar hotel ce da ko titin ta baka isa ka hau ba sai kana wani shege ko dan wani shegen wato rich people. After dinner ko wane ango ya nufi inda Amaryarsa take domin yin hoto da kuma gaisawa da danginta. Ameer ya nufi gidansu Humarah Shuraim kuma ya nufo gidansu Namra Maleek ma haka gida ya dawo domin tasa amaryar yar gida ce.

Wannan ne second time da Humairah ta ji tana jin nauyin daga ido ta kalli mutumen da a yanzu zata iya kiransa da mijinta, yau ne ranar da duk wani buri da take da shi ya cika, a yau hawayenta na farinciki ne Allah ya mallaka mata abun da take da neman zabin Allah akansa, a yau duk wani Ciwon So ya warke zuciya ta samu muradinta hankali kuma ya kwanta. Hannu ya saka ya rika fuskarta ya dago kanta sai ta kasa kallonsa har lokacin hawaye farinciki take, kasancewar babu kowa a falon ya bashi damar kai bakinsa saitin inda hawayenta ke zuba ya sumbance su, sai ta rufe idonta gently ya sumbanci saman fatar idon.

“Yanzu idan na rungume ki babu wanda zai ce akan me, ke ma kuma baki isa ki hana ni ba”

Da wani irin shauki da annurin zuciya yake fadar haka yana kallonta, ta yi irin kyaun da be tana ganin ta yi ba sai yau da take rana ce mai muhimmanci a gareshi. Murmushi ta yi ta rumgume abunta ba tare da ta kalleshi ba, kamshinsa da ba rabo da jikinsa ya rufe ta har sai da ta lumshe ido. Dariya yayi mai sauti ya dagota daga jikinsa sai ya ga idonta a rufe, iskar bakinsa ya busa mata saman idon ya kai bakinsa ya sumbancin hancinta tun tana counting har lissafi ya bace nata, kamin ta ji bakinta cikin nasa sun dade suna musayar yawu sannan ya cire bakinsa ya rumgumeta yana jin kaunarta har cikin ransa. Sun dauki lokaci a haka kamin ya dagota ya sumbance a karo na biyu ya rika hannunta suka fito daga dakin ana ganinsu aka fara dariya ana daukarsu a waya. A falon suka zauna Photographer yana fada musu yadda za su yi, yana daukarsu hoto cikin kunya Humaira take yarda ayi, shi kan gogan daman can ko a lokacin da ba daura ba yayi balle a yanzu da yake jin ko komai yayi mata babu mai ce masa dan me, Ameer irin angwayen nan da ba su da kunya kuma ba sa gudun magana, gashi ya samu shy shy bride.

MALEEK POV.

A hamkali ta shigo falon tana sanye da farin lace ta yafa farin mayafi hannayenta da karfa duka jan lallen ne mai masifar kyau, tana doso inda yake zaune sai ya mike tsaye da farar shadda ce jikinsa an nada masa rawani yana sanye da tsadaddar Alkibbar sarauta dakin sai kamshi kamshin turarensa yake zuwan Nuwaira kuma sai kamshin ya gauraya ya bada wani kalar kamshin na dabam murmushi take tana kallonsa har ta iso inda tsaye yana jiran isowarta.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.