Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel.txt
Chapter 151 of 227
“Ina tunanin yadda Ummi zata tarbe mu ne, bayan duk irin abubuwan da Hajiya take mata”
“Ummi bata da matsala, ba zata miki wulakanci ba, ita da take neman mutane ma, shiyasa na dauki a yanzu ai so nake ku sabu da ita su san juna domin na fahimci kuna da fahimta daya”
Bata sake cewa komai ba, shi ma kuma be yi ta kanta ba tukinsa yake be tsaya ba sai da ya isa gurin wani shopping mall.
“Ina dawowa”
Ya bude motar ya fita, binsa ta yi da kallo har ya shiga Mall din sannan ta sauke ajiyar zuciya. Be jima ba ya fito wani ma'aikacin Mall din yana biye da shi rike da leda biyu, Ameer ya bude back seat aka saka masa ledodin sannan ya rufe ya bude motar ya shiga ya taka motar. Tafiyar ta shiru ce babu wanda ya ce wani uffan har suka isa gidan. Harabar gidan ya faka motarsa ya bude ya fito, sai ta zauna kamar mai jiran ya bude mata ta fito.
“Common fito mana tun da ba ke ce Waira ba, balle ki yi jira na bude miki”
Ta fada da kamar zolaya da wasa, sai da ya yaki zuciyarta sannan ta samu nasarar murmushi ta sake kai hannu ta bude motar ta fito tana karewa gidan kallo. Shi kuma ya rufe gefensa ya bude back seat ya dauko ledodin ya nufi ciki ta ruwa masa baya tana mamakin yadda masu arziki basa jin zafin zuba kudinsa a kasa su gyara muhalli kamar ba za a mutu ba.
[7/24, 5:13 PM] My S Line: 61
Maleek na zaune falon rike da cup din tea sa da Waira ta sha ta aje, Ameer ya shigo falon tare da Humairah. Ko inda suke be kalla ba har Ameer ya nunawa Humaira inda zata zauna, ita kuma ta zauna tana mikawa Ameer gaisuwa. Ya kalleta a tsanake sannan ya amsa mata da kai ta mike tsaye ya fice daga falon. Ameer ya nufi upstairs domin sanar da Ummi zuwansu.
Ummi ta aje numfashi bayan gama sauraren Namra sannan ta ce.
“Mahaifinki ba shi da matsala, tun a kwana baya da na yi masa magana yace zai yi bincike, kuma na tabbatar a yanzu yayi binciken ko kuma yana kan yi, zan sake tuntubarsa na ji”
Namra ta shafa wayarta tana fadin.
“Shuraim din yana ganin kamar Abiey ba zai yarda ya aure ni ba ne, saboda abubuwan da suka faru, yace mahaifinsa ya fada masa komai bayan yayi masa bayanin zuwan da yayi irin tarbar da ya samu da kuma crisis din da suka faru”
Ummi ta kai hannu ya taba kafadarta.
“We're all learners or experts in one way or the other, we're not perfect kowa yana making mistakes kamar yadda ni ma na yi, idan kuma har irin wannan ta kasance be kamata mu dora laifin akan wani ko wata ba, kamar yadda be dace mu bar wasu su cutu ko abun ta shafe su ba, ni dai a ganin da nayi ma yaron nan ina ganin kamar zai yi mutumci da rikon amana, domin akwai natsuwa sosai a tare da shi, after all abun da ya faru still yana bibiyarki yana son a ba shi dama, hakan ya nuna da gaske yake sonki kuma idan kika aureshi zaki jidadi”
“I hope so, nima ina son na yi aure just to make you happy, Ummi you are always telling us burinki a yanzu ki ga aurenmu, Nimra is no more yanzu ni ce kadai hope dinki”
Tana maganar hawaye na sauko mata, Ummi ma kokari ta yi ta hana kanta hawayen amman zuciyarta is melting, babu dare ko ranar da bata tunawa soft hearted lady Nimra, even though mutuwarta ya saka Namra zubar da duk wani ji da kai da ganin ta fi kowa ko banbanta da wasu, daman she's quiet bata son hayani ba kamar Nimra ba dake saurin sabawa da mutane. Hakan kuma ya saka ta kara zama very quiet she talk only when it's necessary.
“Haka Allah ya tsara, dole mu hakura mu karbi kaddara, addu'a ce abar da take bukata a gurinmu yanzu, and i happy for the decision you made, Allah ya hada kanku ya sa mijinki ne har aljanna”
“Ameen”
Ta amsa tare da saka hannu ta goge hawayen idonta. Shigowar Ameer ce ta saka ta mikewa tsaye rike da wayarta ta fice daga dakin ba tare da ce masa komai ba. Ummi ta bita da ido ganin ba su gama tattaunawa ba ta fice saboda shigowar mutumen da take ma kallon makiyinta. Ameer ya kalleta ya dauke kai ya tsaya daga jikin kofar dakin ya kalli Ummi.
“Ummi kina da bakuwa a falo”
Ummi ta dan bude ido try to mai da hawayen idonta cikin idon dan kar ya zubo, ta ari murmushi ya yafa a fuskarta.
“Bakuwa?”
“Eh Humairah ce na kawo miki ku gaisa, zata tafi school na ce bari na zo da ita ku gaisa sai na yi dropping dinta a school din”
“Maa Shaa Allah, aiko ka yi tunani mai kyau kamar ka san kullum burina da tunanina yadda zan kara kusance da alaka a tsakani na da su, ko da yake na lura kakarka bata son kulla wata alaka da ni, wata kila bata shirya yafe min a yanzu ba”
Ameer ya bar jikin kofar ya nufi inda take ya zauna kusa da ita.
“Sometime bama fahimtar abu cikin sauki, ko kuma a kankanen lokaci, wani abun ma sai an mana matashiya an lurar da mu suke gane alfanu ko kuskuren dake cikin abun, dan haka mu bata time ita ma a sannu zata sauko har ku samu fahimta juna. Ai tun da Waira ta yi nasarar tankwara ni na sauko na fahimce ki, na san kowa zai fahimce ke a duniyar nan Ummi, domin na san ni ni a kadan kaina ina da wuyar sha'ani, amman within period of time yarinyar nan ta bude brain dina na fahimci komai, that's why I like her”
Ummi ta kallonsa kawai take da shauki tana jindadin yadda yake nuna son kasancewa da Waira.
“Ina fatar zaka zama haka da sauran yan'uwanka ma, kamar Namra ita ce kadai kanwarku mace a yanzu, amman na lura bakinka da nata be taba haduwa ba tun da ta zo gidan nan”
Ya karkato ya kalleta.
“Ita ya kamata ace tana gaisheni, ko dan ta gan ni zata dauke kai, bayan kuma ni yayanta ne”
“Zan mata magana zata gyara, amman ba daga girma ba ne Allah be ce karami ko babba zai yi zumunci ba, zumunci na kowa ne, idan kuka ce zaki tafi a haka bayan rayuwata ba zaku yi zumunci ba, kuma abun zai fi cutar da Namra a yanzu domin ita ta rasa yar'uwa bata da abokin shawara a yanzu”
“Ya kamata ta girmamani then”
“Zan yi magana da ita, amman kai ma ya kamata ka girmama na gaba da kai, misali Abiey ko da ace ka girme shi ya kamata ace ka girmamashi saboda yana aurena, amman da rana daya baka taba zuwa ka gaishe shi ba, na ga ko ba komai ya girmeka ai kuma ya haifi kamar ka, sannan yana aurena”
Ameer ya hade yawu.
“Shi ma be taba kwatanta zuwa ya dubani ba a bangarenki, tun da na zo gidan nan ban taba ganinsa a bangaren nan ba, be shigo ya tambaye ya nake ba, idan Maleek ne ko Mahmood zai masa haka? Hajiya ta fada min komai akan Abiey irin kiyayyar da ya nunawa mahaifina, hakan ma sai ya saka na kara yi miki uzuri wata kila yana daga cikin mutanen da suke cilasta miki rabuwa da ni, Hajiya ta fada min Abiey baya son mahaifina ko kadan, wata kila kiyayyar mahaifina ce ta shafe ni nima ya tsane ni”
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.