Complete Hausa Novels

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 51 of 227

“Allah sarki Allah yasa tsare ki Waira Waira”

Ya maimaita sunan a karo na farko bayan idonta, ya kalli inda ta cije shi a hannu har ya fasa yana murmushi zuciyarsa sam bata masa dadi, ya san abu ne mai wahala kamin ya manta da lamarinta ba nan kusa ba.

“I hope zaki samu gurin da zaki aminta da kowa, Allah ya hana masu niyar cutar da ke su cutar da ke”

Kamar marar lafiya haka ya wuni a ranar saboda rabuwa da Waira, wata kila da sun dade a tare da ba zai ma iya sabuwa da ita ba saboda shakuwa. Musamman da ya je asibitin suna da zancenta wasu kuma na tambayar abun da ya faru bayan barin asibiti.

©Khadeeja Candy
   ©®Copyright
        2023
[6/17, 10:49 PM] My S Line: *W_G -it's not free, pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*

22

Ummi ta yi saurin shiga tsakiyar su tana kallon Maleek dake huci abun da ba halinsa ba.

“Bata san komai akanka ba, ba ta yi hakan da ganganci ba, bakuwa ce miyasa baka yi wannan tunanin ba?”

Ya dauke kai ba tare da yace komai ba ya shige dakinsa, gaba daya manta yayi abun da ya kawo shi dakin har sai da ya zauna na tsawon lokaci sannan ya mike tsaye, sai ya ji kansa na mugun sarawa irin jikinsa jikinsa yayi weak sosai a take zazzabi ya karyo masa, daker yayi alwala a dole dakin yayi sallah Magariba yana gamawa ko addu'a be tsaya yi ba ya hau gado ya kwanta ya lulluba saboda sanyin da yake ji. Ummi ta kama hannun Waira ta koma da ita cikin dakin tana fada da Nimra wacce ta biyota a guje.

“Ummi na shigo na samu bata kan gadon, i just want to check on her ashe ta boya bayan curtains sai da na daga na ganta ina mata magana na rika ta sai ta fisge ta fito a guje”

“Gashi ai kin tsoratata, kuma kin ja mata ta sha mari ji yadda bakinta yake jini”

Bandaki Ummi ta shiga da ita ta kunna tap ta tara cup ta tara ruwa ta kai mata a baki, kamar wata tsumma haka Waira ta zama hawaye kawai ke zubo mata, duk inda aka yi da ita sai ta bi, ta kuskure baki kamar yadda Ummi ta nuna mata sai ta zubar da ruwan tare da jini, haka tai ta yi har sai da jinin ya fita sannan Ummi ta tafi dakinta ta dauko brush ta saka man goge baki ta mika mata.

“Zaki iya wanke bakin ko kadan ne? Saboda akwai ciwo a bakin”

“Ummi zafi zata ji fa, saboda brush ne kara dai a kyaleta sai gobe ko jibi sai ta wanke”

“Okay”

Ta hada mata ruwan wanka da kanta sannan ta juyo zata fito sai Waira ta biyo bayanta har lokacin hawaye take, yanzu kam ba kuka rashin marin da Maleek ya mata take ba, kukan barin garinsu da rayuwarta take, yanzu kam ta gane ta yi kuskure mai girma, ta baro mutanen da ta sani kuma take iya rayuwa a cikinsu ta dawo a inda bata san kowa ba, kuma kowa be santa yarensu da addininsu ba daya ba, abincinsu ma ba daya ba.

“Wanka zaki yi”

Ummi ta nuna mata ruwa, sai ta juya ta kalli ruwan ta juyo ta kalli Ummi ta fashe da kuka, a nan hankali Ummi yayi matukar tashin tausayinta ya kara kamata domin ta san bata jin yarenta kamar yadda police din suka fada tun kan a kawo ta, gashi ta samu mari daga Maleek ga kuma rashin sabo da su da bata yi ba, domin farkowa kenan ta ganta a dakin akan gado sai sanyin ac, hakan ya saka ta tashi ta boya a bayan lalulen dakin har sai da Nimra ta shigo ta ganta, a kokarinta na gujewa Nimra ne ta fito dakin a guje saboda barin kofar dakin a bude da Nimra ta yi.

“Wani abu na miki ciwo ne?”

Ummi ta taba hannunta sannan ta taba shafin fuskarta a inda Maleek ya mareta gurin har ya kumburo yayi mata ja kasancewar fara irin farin nan da ko sauro ya cijeta sai jikinta ya bayyana.

“Yi hakuri, hakan ba zata sake faruwa ba na miki alkawari”

Ita dai kallon Ummi kawai take ba dan tana jin yarenta ba, ita ma Ummin tana kokarin fahimtar da ita abun da take fada ta hanyar amfani da hannu, sannan ta saka duka hannayen ta goge mata hawayen.

“Ki yi wanka sai a kawo miki abinci”

Da kallo ta bi Ummi har ta fice daga bathroom din tare da Nimra suka ja mata kofar, ba su bata son wanka ba ita kuma bata san yadda zata fada musu cewar bata son wankan ba, tsoro take kar wani ya sake dukanta bata son ta sake yi ma kowa musu a yanzu. Dukawa ta yi a gurin ta rumgume kanta tana hawaye, gaba daya rayuwar da suke da Eid sai ta dawo mata sabuwa, yadda take hawan itace ya tsallaka tsauni, Eid yayi mata busa ta yi rawa sai ta ji tana marmari hakan.
A hankali ta daga kanta tana kallon bathroom din ya ci uban wanda ta shiga a gidansu Dr Shuraim, sulalewa ta yi kasa ta zauna ta kai hannunta mai lafiya ta taba gefen fuskarta, tun da take a rayuwarta ba a taba marin fuskarta haka ba, bata san wani abu zafin dukan ba sai a yanzu da ta farka ta sami kanta a gidansu Maleek, tana sauke hannunta ta tuna da takardar da Dr Shuraim ya bata da kuma tufafinta sai ta kalli hannun ta ga babu komai, a take ta fashe da kuka marar sauti tsoron take kar su ji kukanta ku ce za su daketa, a iya fahimtarta ba kowa yake da tausayi a wannan duniyar data samu kanta ba, saboda farko maciji ya cijeta tana ta neman dauki Ameer be taimake ta ba har ta suma, ta farko ta ganta a wani gurin da bata sani ba, wato asibiti suma sun tsikata mata karfen allura a jiki kamar yadda suka saka mata wani karfen na drip a hannu, kuma suka daure mata hannun da macijin ya tsareta, Dr Shuraim ne kawai ta san ya tausaya mata, kanwarsa da mahaifiyarsa ma sun yi mata wanka da karfin tsiya suka gyara mata gashin kanta yana zafi babu ko tausayi, sannan suka yi ma Dr Fada har sai da ya kai ta gurin mutanen nan masu bakin tufafin, a can aka sake soka mata karfe a jiki ta yi bachi bata farka ba sai yanzu a wani gidan na dabam, gashi kuma ta fara cin karo da mari da ya saka jini fita a bakinta, yanzu kuma sun saka ta a nan sun rufe gani take kamar cilasta mata suke sai ta yi wanka, abun da bata kauna kuma bata saba ba, ko ma zata ta yi wanka ba a irin wannan gurin take yi ba.
Kusan awa daya ta bata a bandakin tana zaune a inda Ummi ta barta, banbanci dazun da yanzu dazun a tsaye ta barta yanzu kuma tana zaune ta saka kanta cikin kafafuwa tana hawaye.

“Baki yi wanka ba”

Ta dago da sauri ta kalli Ummi ta girgiza mata kai, ta mike tsaye da sauri tana taba zuben sarkar da Dr ya saka mata a wuya.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.