Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel.txt
Chapter 132 of 227
“Hmmm Hajiya, ke dai kin ganshi kawai amman da can ba haka yake ba, yanzu ne ya canja”
“Ke ma ai na san halinki fitina ta miki yawa”
Ta yi dariya ta nufi gefen gadon Hajiya ta dauki jakarta ta goya, sannan ta yi mata sallama ta fice, tana tafiya harabar asibitin ta ji an kira sunanta.
“Humairah”
Ta dan juyo kadan sai ta yi arba da Likitan dazun, murmushi.
“Doctor”
“Na'am fita zaki yi?”
“Eh makaranta zan je”
“Wace makaranta? Ina kike karatu”
Ya jera da ita suna tafiya.
“Sky King University”
“Ah makarantar manyan mutane kenan, wane course?”
“Microbiology”
“Wow, ke babba ce”
“Kune manya ai”
“Kika ce ba, muje na sauke ki”
“No akwai inda zan biya kamin na wuce”
“Karki damu duk zan iya sama direbanki, kin ga wata rana zan yi alfahari na ce na taba daukar Humairah yar Microbiology a motata, zan ce ta yi min alfama ta shiga motata”
Murmushi ta sake yi ta girgiza kai.
“Bana son zolaya, Likita za'ayi ma alfama?”
“Eh mana ke baki san babba ce ba?”
Bata son jan zancen da tsawo dan haka ta yi shiru bata sake cewa komai ba har suka isa gurin motae yar yayi mai matukar kyau, kana ganinta kasan sabuwar mota ce, sai da ya saka key sannan ta bude front seat ya shiga ta zauna.
AMEER POV.
A Area 2 ya sauke Fiyya gidan wata kawarta da zata yi birthday, sannan yayi driving kansa zuwa gida, tun a harabar gidan yake kallon bakuwar motar da ke fake a compound din. Domin ba ta yi kama da motocin gidansu ba, yanayin yadda akai parking din ma ya fahimtar da ba direbobin gidansu ba ne. Yana wasa da key hannunsa ya shiga falon, sai ya samu Mummy da Ummi zaune, Daddynsa yana kan dayar kujerar fuskarsa dauke da murmushi. Ummi na ganinsa ta mike tsaye kamar karamin ma'aikaci ya ga boss dinsa.
“Ameer ka dawo”
Daddy ya fada, sai ya nufi inda Daddy yake ya zauna yana yi ma Ummi kallon tsanaki, ta yi rama sosai farinta ya wuce na ainahin fatarta wani fari ne mai sheƙar da fata, fatan idonta ta yi fari kana kallonta ka san lafiya bata isheta ba.
“Baka gaishe da Mamanka ba, tun fitarku take nan tana jiranka”
Mummy ta fada tana murmushi, still be ce komai ba, sai kallonta kawai yake. Hakan ya saka Ummi jin wani iri sai ta ji kamar ta tsargu, domin ganin take komai ta yi ma Ameer a yanzu ba zata burge shi ba.
“Na zo ne kawai na ganka, Daddyka ya fada min abin da ya faru, ina addu'a Allah ya tsare gaba, kuma idan ka ba ni dama ina son ni ma naje na dubata for the sake of you”
Ta karasa maganar muryarta na rawa kamar mai tsoron abun da zai fito daga bakinsa. Ya dauke kai sannan ya mike tsaye.
“Lemme drop her home”
Fadar sai sauke ta a gida, abun mamaki ne a gurin Mummy da kuma Mahaifinsa Daddy ya san da be son ganinta ba zai sauketa gida ba, ba ma zai zauna a falon ba, sai dai Daddy be san manufarsa ta yin haka ba, hakan ya saka shi mikewa tsaye tare da kai hannu ya dafa kafadarsa.
“Karka fada mata magana marar dadi please”
Cikin wata siga mai kamar rada ya fada masa haka, Ameer ya girgiza kai.
“Ba abun da kake tunani ba ne”
Yana bashi amsa ya wuce yayi gaba, Ummi ta dauki jakarta zuciyarta na raya mata maybe Ameer zai yi amfani da wannan damar ne ya fada mata karta sake zuwa gidan duba shi. Mummy ta rakota har gurin motar ta tuko kanta, hakan ya saka Ameer barin jikin motarsa ya iso gurinta ya mika mata hannunsa.
“Key”
Ta ciro key a jakarta ta mika masa, ya nufi motar ya bude mata backseat, ta ji kamar ya karramata yayi mata alfarma a cikin daruruwan mutane.
“Hajiya na gode sai anjima”
“Toh Allah ya kiyaye hanya, ni ma zan shigo wani lokacin In Shaa Allah”
“Allah ya nufa”
Ummi ta fada sannan ta nufi motar ta shiga, Ameer ya rufe motar ya zagaya ya shiga mazaunin direba yayi ma motar key. Yana tukin Ummi na hawaye ko da ace ba a cikin dadin rai Ameer zai tukata ya kaita gida ba, ita abun farinciki ne a gurinta.
“Karki sake zuwa duba ni, idan kina son ganina ki min waya zan zo”
Ya fada yana tukin a hankali.
“Ba lallai idan na ce ina son ganinka ka zo ba”
“Saboda me?”
“Saboda ban kyautata maka ba, a lokacin da kake bukatata, na san kana kallona da wannan abun a kullum”
Yayi shiru na tsawon lokaci kamin ya sake fadar.
“Me yasa to kika yi?”
Hannu ta saka ta share hawayen idonta.
“A lokacin ina tsoron rasa rayuwar mahaifinka ne, saboda likitoci sun tabbatar min, idan ba a yi masa aikin ba, zai iya mutuwa, mun siyar da gidan gadonmu da kayan dakin Yayata Maryam mun hada duk be wadatarwa na bi yan'uwana da abokan mahaifina, kowa be taimaka min ba, ina cikin wannan halin ne Dr Hamid ya kawo min mafitar cewar akwai wacce take son siyen ciki, idona a rufe na aminta aka siyar, sai bayan da aka yi aikin mahaifinka sai kuma rayuwa ta yi bankwana, babu yadda ban yi ba saboda na gudu da cikinka amman ban samu dama ba, saboda ina da talaka ba ni da ikon komai, a cikin yarjejeniyar da aka yi da Hajiya Jamila ance idan har na karya alkawari zan biya kudi mai yawa, kuma ba ni da su...”
Ta yi shiru saboda hawaye dake mata zuba suna son su ci karfinta su zame mata kuka.
“Su waye yan'uwa mahaifina? Ban san su ba”
“Idan kana son sani, zan fada maka su, zan tafi da kai har Kano ka gansu”
“Sun san abun da kika aikata?”
“aa ba su sani ba, duniya tana kallon ďan da na haifa da Deen a matsayin mataccen”
Hawaye sun saukowa Ameer, sai ya kara rage gudun motar ya faka gefen titi ya jinginar da kansa jikin kujera.
“I'm sorry, na san baka kaunata na san a gareka ban cika uwa ba, na san ba zan taba kima a idonka ba, amman please don't leave me, i want you here with me, na san ba abu ne mai sauki ba, kuma ban cancanci ko wace kalar alfarma a gareka ba”
“Idan kina bukatata a kusa da ke, you can make a room for me, sai na dawo gidanki na zauna, i need to know who you are, me kike so miye baki so, ya rayuwarki take. It tear me up when you turn me down, ina son na ji ɗumin uwa how it's? To get to know you”
Yana fada yana kuka kamar karamin yaro. Ta girgiza kai.
“I don't want to force you”
Bude motar yayi ya fita ya rufe ya dawo back ya bude ita dai binsa kawai take da ido har ya shigo.
“You didn't force me, ni nake neman wannan alfarmar, ni dai kawai ina bukatar uwa ne, ko da wata uwarce ba ke ba zata tsaya a gabana tace ita ta haife ni, zan karbeta you leave a empty place here in my heart, i want you to fix it, that's little boy you left is still inside me, and he need a mother, i want to make a motherhood memory now”
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.