Complete Hausa Novels

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 161 of 227

“Aa daman akwai wannan maganar tun da dadewa kuma ba wai an yanke hukunci ba ne za a duba aga idan abun da zai a iya ne”

Ummi ta kai hannu ta dafa kirjinsa domin ta lura da yadda ya dauki zafi gaba daya yanayinsa ya sauya. Maleek ya mike tsaye ya nufo inda Ameer yake tsaye yana fadin.

“No ba Saboda haka ba ne, saboda ya isa da ita ne, saboda yana jin shi ya riketa ya yi mata komai a lokacin da ka gudu ka barta kuma ka ce baka santa ba, a yanzu Abiey ne gatanta yana da ikon yayi yadda yake so da ita, a ciki har da yiyuwar duba baka aurenta ko akasin haka, cancantarka ta kai a baka innocent girl like Waira ko kuma aa, so kai ma a karkashin ikonsa kake a yanzu dan haka ka taka a hankali, nan gidansa ne karka manta”

Ameer yayi murmushi ya nunawa Ummi Maleek da hannu.

“You see i told you ai, ba takamarka gida ni da Waira zamu bar muku gidan, sai ka yi yadda kake so, karka manta nine silar zuwanta a nan gidan, idan kuma kudi ne damuwarku then tell me the price i will pay”

Namra ta mike tsaye ta nufo inda yake tana daka masa tsawa.

“Daga baya kenan? Wai Ameer me yake damunka? Taya zaka tsaya a gaban idonmu kana fadar magana son ranka kamar kai kake mulkarmu? Baka da wannan yanci ya kamata kasan da wannan, kuma price din da Abiey ya kashe gurin gina rayuwar Waira ba zaka iya biya ba, domin baka da komai kuma baka yi gadon komai ba sai tsiya, kai ba dan babban attajirin da kake kallo a matsayin uba ba ne a yanzu, kai dan talaka ne jikanta talaka jikar tsohuwar dake bara a titi, kuma dan uban da aka rasa kudin aikin mahaifinsa har sai da aka siyar da cikinsa you're nothing Ameer but pieces of trash...”

Tana kai aya Ummi ta kai hannu ta juyo da ita ta wanke mata fuska da mari hudu masu kyau, sannan ta nuna ta da yatsa jikinta na rawa ta ce.

“Ban yafe ba, idan kika sake fadawa Ameer wata mummunar kalma makamanciyar wannan Allah ya isa tsakanina da ke...!”

Maleek da ke tsaye gafen Ummi tana kallonta da mamaki ya ce.

“Ummi akan Ameer din?”

Tasaaaass kake ji Ummi ta bashi na sa kason na mari.....
[7/27, 5:45 PM] My S Line: 65

“Ummi you slap him...?”

Mahmood ya fada with shock yana kallon Ummi.

“Duk abun da kuke yi, ba Ameer kuke yi ma ba, ni kuke yi ma, saboda ni komai ya faru, idan zaku ci mutumcin Ameer ku fuskance ni kai tsaye ku ci mutumcina amman ba Ameer ba, idan baku kaunaci junanku a yanzu da nake raye ba when zaku so junanku? Bayan na mutu? When when when?”

Ta tambayi Ameer ta tambayi Maleek ta tambayi Namra dake dafe da kunci tana hawaye.

“Kwana nawa ya rage min? Kullum kokarin gada kanku nake amman sai kara bandarewa kuke yi? Ni haka zan gama rayuwa cikin bakincikin yaya? Why? Kuma ace duk saboda mace kuke wannan abun? Ni kadai ce uwa? Ba ku san abun da yake damuna ba, a kullum kara min bakinciki kuke”

Maleek ya sauke ajiyar zuciya a hankali.

“I'm sorry Ummi ban yi saboda na bata ranki, abun da Ameer yayi ne ya wuce hankali, please forgive me amman zan tabbatar masa da cewar be isa ya dauke Waira daga gidan nan ba, ko da kuwa hakan na nufin yaki”

Fita yayi daga falon bayan gama fadar hakan, Namra kuma ta haye sama tana kuka sosai. Mahmood ya watsawa Ameer wani banzan kallo ya fice a fusace. Sai aka bar Ameer a tsaye jiki babu karfi kamar wanda aka sarewa gaɓoɓi ya kasa motsawa daga inda yake saboda gorin da Namra da Maleek suka masa ta ce. Ummi ta kalleshi a hankali tana hawaye.

“Are you happy now? Dan farinciki da kowa ya tashi da safen nan ka wargaza shi, ga breakfast dinka can ka ci kafin ka fita”

Ta zagaye shi ta haye sama, tana shiga dakinta ta dauki wayarta ta kira Ya Maryam domin take kallo a matsayin uwa a yanzu kuma ita ce abokiyar shawararta. Ya Maryam ta numfasa bayan ta gama sauraren Ummi ta soma bata shawarar abun da take ganin zai fi zame mata mafita.

“Ba zaki iya zabe wa zai aureta a cikin yayanki ba, kuma irin wannan rashin jituwar dake tsakaninsu zai iya haifar da gaba da kiyayya da zata shafi yayansu kuma ta cigaba da bibiyarsu har bayan rayuwarki, ni dai a nawa ganin karki bari kowa ya aureta a cikinsu”

“Ni ma na yi wannan tunanin, kuma abun da ya faru a yau ina yi ma Ameer uzuri, a yadda na fahimta yana da saurin fushin zuciya, kuma a yadda Waira ta fada masa kai tsaye za a kaita waje karatu dole yayi zaton saboda shi ne, na san be kamata yayi magana a tsaye ba, amman....”

Ta yi shiru. Ya Maryam ta ce

“Zahra kina son Ameer da yawa ko ba haka ba?”

“Ko wane ďa da irin yadda Allah yake dorawa uwa soyayyarsa a zuciyarta, Ya Maryam ina jin kamar na cutar da yaron nan, ina jin kamar rashin kasancewarsa a kusa da ni ne ya haifar duk wani hali da yake ciki, wata kila da yana tare da ni da haka be faru ba, kuma idan ban so Ameer ba waye zai so shi? Mahaifinsa be raye a yanzu, Abiey baya son Ameer ko kadan na lura da haka, a dan lokacin da ya rage min ina son na kyautata masa, ko da shi zai munana min idan bana raye zai yi nadama kuma zai gane na nuna masa soyayya”

“Haka ne, maza da yawa basa son ƴaƴan matansu, kalilan ne suke so, balle kuma Abiey da yake da riko da kasa manta abubuwa, sai hakuri”

“Amman su mata suna son yayan mazanjensu ko? Na rike nasa yayan kamar nawa, hakan be isa ya saka shi son Ameer ba?”

“Rayuwar namiji dabam take da ta mace, haka ma zuciya kuma hakan ba yana nufin baya sonki ba, na fi kowa sanin Abiey na kaunarki”

“Maso uwa ya so ďandanta Ya Maryam, idan bana raye alaka zata yanke tsakanin yayan Abiey da Ameer”

“Dole ki jajirce ki ga komai ya daidaita tsakaninsu, saboda gaba, kuma ina son na ja hankalinki karki sake yi ma dayansu irin wannan hukuncin na duka a gaban Ameer, idan ma zaki yi to ki kebe kowa dabam Kuma ki saka addu'a a gaba kina rokon Allah ya hada kan yayanki nima zan taya ki, ina nan zuwa satin sama In Shaa Allah”

“Toh Ya Maryam Na gode Allah kawo ki lafiya”

Daga haka suka yi sallama. Ummi ta aje wayar ta mike tsaye ta shiga bedroom ta wanke fuskarta ta fito gyara daurin dankwalinta sannan ta fice daga dakinta zuwa dakin Waira har lokacin kuka take idonta ya kumbura sosai har wani numfashin take sama_sama saboda kukan da take. Ummi ta karasa cikin dakin ta zauna bakin gadon Waira a yayinda Waira take zaune kasa, this is the first time da ta ji bata son zaman Waira a gidan ba dan ta gundira da ita ba sai dan matsalar da zamanta a gidan zai haifar ga ƴaƴan da take neman hadin kansu.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.