Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel.txt
Chapter 12 of 227
“Miyasa za mu zauna a nan wai?”
Tarig ya tambaya domin basa jin sakewa a public place like this one.
“Ban cilastawa kowa zama ba, ni kuka tarar a nan zaune kuma kuka yi deciding ku zauna, zaku iya shiga ciki idan kuna ra'ayi”
Ya fada tamkar ba shi yake maganar ba, ya tattara hankalinsa gaba daya ya maida gurin mutane dake kai da kawo a gurin.
“Ameer ya kamata ku sasanta kanku da Maleek”
“Miyasa na zauna a nan”
Ameer ya fada da sauri yana rufe idonsa domin ko maganar Maleek baya so. Tarig da yayi maganar ya kalleshi da mamakin jin furuncin da be tsammaci jinsa daga bakinsa a yanzu ba.
“Kana nufin saboda ku shirya ka zauna a nan?”
“Saboda mu kara nisantar juna dai, bana son ko gurin da na zauna Maleek ya sake zama”
“No Ameer wannan dabi'un yara ne, mu kuma ba yara ba ne, be kamata mu yi haka ba?”
“Idan ka sake min wata maganar da ta shafi Maleek Tarig sai na hada kai da shi na bindigeku, baka san yadda yaron nan ya bata min rai ba ko? Kawai yawu ya watsa min a fuska fa haba”
Ameer ya fada babu alamar wasa a fuskarsa. Tarig ya wasa masa wani kallon banza.
“Go ahead waya rike ka? Ka saka bindigar ka halbemu mana sai ka gani idan kai zama zaka yi a duniyar, kai babu wanda ya isa ya fada maka gaskiya ko ya nuna maka abun da kai ba ba daidai ba ne, wane irin girman kai ne a tare da kai?”
“Irin wanda ba a siye da kudi balle ka siye, kuma ba a saukewa balle ka raba ni da shi, ya zaka yi?”
Kallon kallo akuya kallon kura suka rika yi ma junansu. Kamin Ameer ya mike tsaye yana ya nufi motarsa hango Maleek ya fito daga motarsa ya doso gurin. Maleek ya kalli Ameer kamar ya yi masa magana domin shi baya son gaba kuma be iya gaba ba, duk yadda zaka bata masa rai sai yayi maka magana, sai dai kuma wata zuciyar ta hana shi gudun kar Ameer ya disgashi a gaban jama'a.
“Tafiya yayi?”
Maleek ya fada a yayinda yake kokarin zama. Tarig ya sauke ajiyar zuciya ya ciro wayarsa aljihu ya soma tabawa yana fadin.
“Wani lokacin na kan rasa gane kan Ameer, yana da fushi sosai kuma yana dadewa be sauka ba, kai ma kuma abun da ka yi baka kyauta masa, na san yadda ya tsani kazanta taya zaka tofa masa yawu a fuska”
Maleek ya hade yawu na rashin jindadin abun da yayi.
“I know that's why I'm here hakuri na so na ba shi, kuma shi ma ya kamata ace yana kiyaye abun da bana so”
“idan wani ya ciza sai wani ya hura, ba wai kai ka yi fushi ba shi yayi fushi, dukamu tare muke ba zamu zabeka mu cireshi a cikinmu ba, haka kuma na za mu cireka mu zauna da shi”
A kokarin Maleek na kawar da maganar ya tambaye dayan abokin na su.
“Ina Abdull?”
“Be zo ba”
“And miyasa kuka zauna a nan?”
“Ameer na tarar a nan, baya son shiga ciki saboda kar ku zauna a guri daya”
Maleek yayi murmushi mai sauti
“Yara ne suke wannan, of course zamu yi fada mu batawa juna rai amman ban da gaba ko tsanar juna ko kyamar zama kusa da juna”
Maleek ya fadar hakan Dawood da ya karaso inda suke zaune ya daki kafadarsa yana dariya.
“That's right bro, zaman da babu fada ba taren amana ba ce, zo mu zauna shi ne zo mu saba dole ne mu rika hakuri da juna”
Maleek ya mika masa hannu suka gaisa, kana suka mike tsaye gaba dayansu suka shiga can cikin VIP din suka zauna, wani sabon shafin hira ya bude, waiter dake kawo musu lemu ya kawo tare da zubawa kowa a cups dinsa sannan ya aje ragowar, ya koma gurin aikinsa Maleek ne ya fara dauka ya sha domin coconut drink ne favorite dinsa, sannan Dawood ya sha, an jima kadan aka kawo musu abin tabawa kowaya ci ya sha, daman Ameer ne kawai baya ci ko shan wani abu a gurin saboda tsabdar da yake da ita, wai shi ba zai iya cin abincin restaurant ba domin be san iya sharing din da aka yi da spoon din ko plate ba, and be san wadanda suka girka ba, kuma ba shi da tabbacin an tsabtace girkin ko akasin haka.
After like 20 min da shan lemin Ameer ya ji kansa na masa nauyi har yana saukowa cikin idonsa, ba kuma ciwo yake jin kan na masa ba nauyi yake irin na wadanda bachi be wadace su ba, sai dai ya daure duk hirar da ake be nuna komai ba duk da kasancewar baya cewa komai sai kallonsu yake yana murmushin karfin hali.
“Hey Bachi kake ji?”
Tarig ya tambaya lura da yadda Ameer yake lumshe ido yana budewa a kokarinsa na hana kanshi bachin da be san ta ina yake fito masa ba.
“Maybe”
Ya fada cikin rashin tabbacin idan bachin ne domin ya san yayi enough bachi jiya. Ya mike tsaye ya dauki keys dinsa dake kan table din
“Bari na tafi”
Be jira cewarsu ba ya fice daga gurin yana jin idanuwansa na kara nauyi har baya son daga su sosai, kamin ya isa gurin motarsa har wani jiri jiri yake ji yana dibarsa kamar zai fadi, lalabe yayi ta yi kamin ya samu sa'ar saka key din motar a muhallinsa ya bude ya shiga sai ya dora kansa saman sitiyarin motar yana ta kokuwa da bachin mai kama da na sihiri.
“Malam lafiya?”
Ya ji wata muryar wanda ta yi masa kama da muryar da ya sani tana kokarin shigowa a cikin birnin dake kokarin gina duniyarsa a bachinsa, ba karamin shahada yayi ba sannan ya samu bude idon da suka soma sauya launi ya kalli fuskar kyakkyawan saurayin da ba zai wuce sa'ar kanensa Mahmood ba.
“Lafiya kalau Bachi nake ji”
“Subhanallah zaka iya tuka motar kuwa”
“Shi ne abun da nake tunani”
“Bari na taimaka maka, ka koma gaba zai na motar ina ne gidanku?”
Kamin ya amsawa bakon saurayin har bachin ya ci karfinsa ya tafi da idonsa har sai da saurayin ya jijjiga kafadarsa.
“Malam... Ka koma dayan side din”
Daker ya rika kofar motar ya fito yana tafiya kamar marar lafiya mutumen ya zagaya ya bude masa from seat Maleek ya shiga ya zauna, har yana masa godiya. Kamin saurayin ya zagaya ya shiga mazaunin direba har bachin Maleek ya fara nisa.
Saurayin dake sanye da kannan kaya ya tashi motar suka hau titi, minti biyu uku sai saurayin ya juya kalli Maleek dake ta bachi, unguwanin da babu mutane ya nufa da shi sai da ya lura da gurin da mutane ba za su ganshi ba sannan ya faka motar, ya ciro wayarsa ya shiga camera ya kunna, ya cire rigar jikinsa ya dago daga jikin tasa kujerar ya kwanto a ta Maleek ya fara sumbantarsa, yana shafa jikinsa.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”
Maleek ya fada jin wani bakon yanayi da be taba jin irinsa ba, ya daga idonsa daker ya sauke su cikin na saurayin bakinsa ke hade da na shi, hancinsu yana gogar juna.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.